Tirkashi! Ashe wannan Dalilin ne Yasaka Abba Gida Gida yake Rusa dukkan Ayyukan da Ganduje yayi
wannan Dalilin ne Yasaka Abba Gida Gida yake Rusa dukkan Ayyukan da Ganduje yayi.
Yanzu-yanzu: Gwamna Ganduje ya yiwa Abba Gida-gida fatan Alheri, amma ya ce za su haɗu a Kotu
Haka zalika Abba gida gida ya bayyana dalilin da yasa yake rusau.
Zaku iya Jin Cikekken Bayanin ta haryar danna hoton bidiyo dake kasa
PLAY ▶️
Yanzu-yanzu: Gwamna Ganduje ya yiwa Abba Gida-gida fatan Alheri, amma ya ce za su haɗu a Kotu
Gwamnan Kano Abdullahi Umar Ganduje, ya yiwa zaɓaɓɓan Gwamnan Kano Engr Abba Kabir Yusif fatan gudanar da Gwamnati yadda ya kamata.
Gwamna Ganduje ya bayyana hakan a yau Asabar bayan kammala Addu’ar neman zaman lafiya da ci gaban jihar Kano da kuma yiwa shugaban zaɓaɓɓen Shugaban ƙasa Bola Ahmad Tunubu, Addu’ar fara mulki cikin nasara a wani ɓangare na tayashi murnar cika shekaru saba’in da ɗaya a Duniya.
Bayan kammala taron Addu’ar a ɗakin taro na Africa house dake Gidan Gwamnati.
A jawabinsa cikin harshen turanci Gwamna Ganduje ya ce nasarar da Engr. Abba Kabir Yusif ya samu ta wucin gadi ce kuma zasu ƙalubalance ta a kotu.
Gwamnan ya kuma ce zasu kafa kwamitin mika mulaki cikin salama.
Wakilinmu a fadar Gwamnatin Kano Abba Isah Muhammad ya ruwaito cewar taron Addu’ar yasamu halartar Malamai maza da Mata na Tijjaniya da Ƙadiriyya dana Izala.
Comments
Post a Comment